Showing posts with label News. Show all posts
Showing posts with label News. Show all posts

Na Cika Alƙawarin Da Nayi Na Raba Takin Zamani Kafin Saukar Damunar Bana - Gwamna Raɗɗa




Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya bayyana haka ne, a ranar Litinin  05/05/2025, a lokacin da yake ƙaddamar da fara siyar da takin zamani ga manoman jihar Katsina, na damunar bana wanda yawan shi ya kai tan 20,000 a ƙaramar hukumar Kusada.

Da yake gabatar da jawabi gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda PhD,CON, ya shaida ma al'ummar jihar Katsina cewa " irin  wannan tallafin da muka samar a damunar bara ya bunƙasa amfanin gona sosai ga manoma.

Ya ƙara da cewa kamar yadda nayi alƙawarin bayar da takin zamani na damunar bana kafin saukar ruwan sama, cikin ikon Allah yau na cika wannan alƙawari, domin inganta noma da wadatar da abinci a jihar Katsina, kuma ina kira ga manoman da su riƙa amfani da dabarun noma na zamani domin bunƙasa noma.

Ya cigaba da cewa zamu kai wannan taki ne a kowace rumfar zaɓe da ke wannan jihar, kuma za'a siyar da takin a farashi mai sauƙi na rabin kuɗin da ake siyar da shi a kasuwa.

Gwamnan yace bayan takin zamani da zamu raba wanda ya kai buhu 400,000, kwana biyu da ya gabata shugaban ƙasa Asiwaju Bola Tinubu, ya ƙaddamar da cibiyar samar da kayan aikin gona mai ɗauke da taraktoci 400 da sauran kayan aikin na zamani kuma kowace ƙaramar hukuma zata amfana da taraktocin nan.

Ya cigaba da cewa wannan taraktoci za'a riƙa bada su haya ne ga manoma, kowane manomi zai amshi haya, idan ya kammala amfani da ita sai ya dawo da ita, kuma mun yi hakan ne domin kauce ma abun da ke faruwa a baya wasu manya su handame ko a siyar da su wata jiha.

Daga ƙarshe Gwamnan ya bayyana irin muhimman ayyukan da yayi a jihar Katsina domin kawo cigaba a jihar, wanda suka haɗa da bunƙasa cibiyoyin kiwon lafiya a matakin farko, ilimi, magance matsalar tsaro, da sauran su.

A jawabin shi Kwamishinan gona na jihar Katsina Farfesa Ahmed Muhammad Bakori, ya bayyana gwamnan jihar Katsina ya samar da takin ne domin inganta noma a jihar Katsina.

Ya cigaba da cewa noman damuna shine noman da al'ummar jihar Katsina suka fi dogaro da shi, sabo da haka wannan takin zai bada gagarumar gudummuwa domin cigaban noma, kuma wannan yinƙurin yana daga cikin ƙoƙarin gwamna na bunƙasa noma.

Tun da fari shugaban ƙaramar hukumar Kusada Hon. Sani Aminu Dangamau, ne ya fara jawabin maraba, inda ya bayyana kawo ƙaddamar da takin ƙaramar hukumar shi abun alfahari ne, kuma ya yi kira ga al'umma da su kauce ma karkatar  da takin zuwa hanyar da bai dace ba domin kauce ma fushin hukuma.

Shugaban ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin jihar Katsina Hon. Rabo Tambaya, ya yi jawabin godiya a madadin ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin, inda ya bayyana jin daɗin shi ganin yadda gwamnan ya yi abun da zai taimaki noma a jihar Katsina, yace samar da takin zamanin a lokacin da ya dace abu ne da zai taimaki manoman jihar Katsina.

Shima a nashi jawabin shugaban kamfanin takin zamani na Boko "Boko Fertilizer" Muhammad Sambo Alhassan, ya jinjinawa gwamna Raɗɗa bisa samar da takin zamanin ga al'ummar jihar Katsina bisa farashi mai sauƙi, ya kuma ce samar da takin zai bunƙasa noma, tattalin arziki, da samar da aikin yi a jihar Katsina.

Wanda suka halarci taron akwai Kakakin majalissar dokoki wanda ya samu wakilcin shugaban kwamitin noma na majalisar, shugaban ma'aikatan gidan gwamnati Hon. Abdulkadir Mamman Nasir, sakataren gwamnan Hon. Abdullahi Aliyu Turaji, ƴan majalissar zartaswa, da sauransu 

HAjj 2025||Gwamna Radda ya k'addamar da tawagar jihar katsina zuwa kasa mai tsarki

 G



wamna jahar katsina malam Dikko Umar Radda, ya k'addamar da tawagar da zata jagoranci aikin hajjin bana, inda ya nada mataimakinsa malam Faruq Lawal jobe, a matsayin Amirul Hajj.

Tawagar ta kunshi kakakin majalissar jihar katsina Nasir yahaya Daura wakilai daga majalissar masarautar Daura katsina da kwamishina Harkokin Addinai Alh. Shehu Abubakar Dabai, da wasu jamia'n gwamnati da malamai.

Gwamna Radda ya bukaci tawagar da su sa ido kan dukkan ayyuka da tsare tsaren da suka shafi jin dadin maniyyata sauka da tashi su, da kuma dawo da su gida lafiya.

Ya ja kunnan malamai da aka dauka daga kananan hukomomi da su gudanar da waazi cikin gaskiya yana mai  cewa Gwamnati ta kashe kudin jama'a wajan daukarsu don haka ana bukatar suyi aiki da rikon Amana.

Haka kuma ya umarci hukumar aikin hajjin da ta tabbatar da cewa duk ma aikatan da aka dauka sun sauke nauyi da aka dora masu, tare da daukar mataki kan wadanda basu ciki aiki ba.

A jawabin sa na godiya Amirul Hajj kuma mataimakin Gwamna malam Faruq Lawal jobe ya tabbatar da cewa tawagar za tayi duk mai yiwuwa wajan ganin an gudanar da aikin hajjin bana cikin nasara da tsari.

Ya kuma roki Allah daya basu nasara a cikin aikin hajjin na shekarar 2025.

Mataimakin Gwamnan jihar Katsina ya gabatar da taron manema labaru kan bunƙasa ilimi a jihar Katsina


 


Malam Faruq Lawal Jobe ya gabatar da taron manema labarai na wata-wata a ofishinsa da ke tsohuwar gidan gwamnatin Jihar Katsina.a

A yayin taron, ya jaddada cewa gwamnatin Jihar Katsina ta mayar da hankali kan ci gaban ilimi, inda ya bayyana cewa gwamnatin jihar karkashin jagorancin Malam Dikko Umar Radda ta dukufa wajen inganta ilimi domin samar da ingantacciyar makoma ga al'ummar jihar.

Ya kara da cewa tun daga matakin firamare har zuwa manyan makarantu, gwamnati ta zuba jari mai yawa don tabbatar da ingancin koyo da koyarwa. A cewarsa, gwamnatin ta kashe biliyan N9.1 ta hannun Hukumar Ilimin Firamare ta Jihar Katsina (SUBEB) domin gina sabbin ajujuwa 160 da gyara 258. Haka nan, an samar da rijiyoyin burtsatse 81, bandaki 46, tare da gidajen malamai 20. Bugu da kari, an samar da kujerun malamai 612 da kuma kujerun dalibai 14,602.

Mataimakin gwamnan ya kuma bayyana cewa an kashe biliyan N5.6 karkashin shirin TIS domin gina sabbin makarantu 150 tare da samar da wutar lantarki ta hasken rana, rijiyoyin burtsatse, da kuma kayan koyarwa.



An ƙaɗdamar da taron bada tuta ga ɗan takarar shugabancin ƙaramar hukumar Katsina A ranar laraba 29 ga watan Janairu 2025 Dan takarar shugabancin karamar hukumar katsina a jam' iyyar APC HON ISAH MIQDAD AD SAUDE tare da sauran masu ruwa da tsaki na karamar hukumar katsina suka jagoranci mika tutar yakin neman zaben a filin Kangiwa dake ƙofar soro Kwamishina ma' aikatar ruwa na jihar katsina HON BASHIR GAMBO SAULAWA shine ya jagoranci kwamitin masu ruwa da tsaki domin mika tutocin yakin neman zaben a filin kangiy dake kofar soro da yake gabatar da jawabi bayan kammala basu tutocin Dan takarar shugabancin karamar hukumar ta katsina HON.ISAH MIQDAD AD SAUDE ya fara da mika sakon godiya ga illahirin masu ruwa da tsaki na karamar hukumar katsina wanda suka halarta Dama Wanda basu samu damar zuwa ba bisa irin taimakon da kuma gudunmawar da suke basu ya kuma roki al' ummar karamar hukumar katsina dasu fito ranar zaben Ya kuma yin kira ga Al'umma na ƙaramar hukumar ta Katsina da fito domin maida biki musanman duba da la'akari da irin ayyukan da maigirma Gwamana jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya aiwatar A jihar Katsina

 



A ranar laraba 29 ga watan Janairu  2025 Dan takarar shugabancin karamar hukumar katsina a jam' iyyar APC HON ISAH MIQDAD AD SAUDE tare da sauran masu ruwa da tsaki na karamar hukumar katsina suka jagoranci mika tutar yakin neman zaben a filin Kangiwa dake ƙofar soro 

Kwamishina ma' aikatar ruwa na jihar katsina HON BASHIR GAMBO SAULAWA shine ya jagoranci kwamitin masu ruwa da tsaki domin mika tutocin yakin neman zaben a filin kangiy dake kofar soro da yake gabatar da jawabi bayan kammala basu tutocin Dan takarar shugabancin karamar hukumar ta katsina HON.ISAH MIQDAD AD SAUDE ya fara da mika sakon godiya ga illahirin masu ruwa da tsaki na karamar hukumar katsina wanda suka halarta 

Dama Wanda basu samu damar zuwa ba bisa irin taimakon da kuma gudunmawar da suke basu ya kuma roki al' ummar karamar hukumar katsina dasu fito ranar zaben 

Ya kuma yin kira ga Al'umma na ƙaramar hukumar ta Katsina da fito domin maida biki musanman duba da la'akari da irin ayyukan da maigirma Gwamana jihar Katsina Malam Dikko Umar Raɗɗa ya aiwatar A jihar Katsina

Hon. Isah Miqdad AD Saude Ya Yara Jaddada Niyar Shi Ta Tallafa Ma Al'umma

Hon. Isah Miqdad AD Saude ya ķara jaddada aniyar shi ta tallafa ma al'umma babu dare babu rana a ranar Laraba 22/1/2025.

 AD Saude ya ķara ķaddamar da rabon kayan karatu ga đaluban Primary su dubu đaya 1000 daga mabam-bantan Makarantu guda 24 dake a ķaramar hukumar Katsina. 

Sudai wađannan Đaluban an zakulo su ne daga Mazabu  12, da muke da su a ķaramar hukumar ta Katsina. 

Shugaban Kwamitin Ilimi, Malam Isma’il Tukur Taury, ya bayyana yadda aka tsara shirin.

Kayan karatun da aka raba sun hađa da Littattafai guda 1000 da Jikkunan 'yan Makaranta suma guda 1000 tare da kwalayen Alli wanda kowane kwali akwai fakiti guda 20 a ciki, daga ķarshe sai akwattan agajin gaggawa (First aid box), wađanda suma adadin su ya kai su 30 suma kuma cike suke da magunguna kala-kala a cikin su. A matakin sakandare kuwa, an bayar da tallafin karatu ga dalibai 48 wanda zai dauki nauyin karatunsu har zuwa kammalawa a shirin farko. Baya ga haka, dalibai 222 daga makarantu na Community School sun amfana da kayan karatu da tallafin sufuri.

Shugaban Hukumar Tallafin Karatu ta Jihar Katsina, Dr. Aminu Tsauri, ya yabawa shirin, yana mai kwatanta shi da hangen nesan Gwamna Dikko Umar Radda. Ya kuma bayyana cewa hukumar ta ware makudan kudade domin tallafawa dalibai, har da tura wasu zuwa kasashen waje domin karatu.

Haka zalika, dan majalisar dokokin jihar Katsina, Hon. Ali Abu Albaba, ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da su shiga cikin harkar tallafawa ilimi. Fitaccen dan siyasar Katsina, Alhaji Ido Kwado, ya tabbatar da goyon bayansa ga wannan shiri, yana mai bayyana shi a matsayin wata babbar dama ga al’umma.

Kungiyoyi kamar su Dikko Project, Lamido Foundation, da Gwagware Foundation sun bayar da tallafi domin kara wa shirin kuzari tare da saukaka zirga-zirgar dalibai.

Taron ya kasance kashi na uku cikin shirye-shiryen tallafin ilimi da Isah ya gudanar, wanda ya kara tabbatar da jajircewarsa wajen gina al’umma mai ilimi a karamar hukumar Katsina.

Wannan taron ya gudana ne a Kambarawa Primary school dake kan babban titin zuwa Daura, cikin garin Katsina. 

Mai girma uban taro Isah Miqdad yayi kira ga đalubai da Malaman da zasu amfana da wannan tallafin da suyi amfani da shi ta hanyar da ta dace, domin ta hakan ne suma zasu amfani al'umma nan gaba. 

Daga ķarshe Miqdad ya yaba ma al'ummar da suka halarci taron maza da mata musamman manyan baķi wađanda suka hađa da Abu Ali Albaba, Alhaji Idi Kwado (Sarkin Aiki), Alhaji Musa Gafai, Alhaji Dahiru Danmarna, Alhaji Lolo Dakare da sauransu.

KATSINA NSCDC ARRESTS KEDCO STAFF FOR TRESPASS, METER TAMPERING, AND THEFT IN DAURA

 

KATSINA NSCDC ARRESTS KEDCO STAFF FOR TRESPASS, METER TAMPERING, AND THEFT IN DAURA

The Katsina State Command of the Nigeria Security and Civil Defence Corps (NSCDC), under the leadership of Commandant Aminu Datti Ahmad (FSF, MADM), continues to demonstrate its commitment to safeguarding lives, property, and socio-economic stability in the state.

In line with these efforts, the Command has apprehended Aliyu Muhammad, a 38-year-old staff member of Kano Electricity Distribution Company (KEDCO), Prepaid Meter Unit, Daura Regional Office, for trespass, tampering with a prepaid meter, and theft. The incident occurred on Thursday, January 16, 2025, at Tudun Wada Quarters, Daura Local Government Area.

The suspect unlawfully removed a prepaid meter from the residence of Alhaji Lawal Gadi. He was arrested by the surveillance team attached to the Daura Divisional Office, led by CSC Bashir Umar Fago, and transferred to the Command Headquarters for further investigation.

During interrogation, the suspect admitted to the crime, revealing that he had surveyed the area on Wednesday, January 15, before returning the following day to execute his plan. The stolen prepaid meter was recovered and is now in custody as evidence.

The Commandant emphasized that acts of vandalism, theft, and property tampering threaten the socio-economic fabric of society and will not be tolerated. The NSCDC remains vigilant, maintaining 24-hour surveillance to combat such crimes across Katsina State.

Commandant Ahmad thanked the public for their ongoing cooperation and urged them to provide actionable intelligence to security agencies to help uncover criminal activities. The Command remains steadfast in ensuring a safe and secure environment for all residents of Katsina State and Nigeria at large.

E-Signed

SC Buhari Hamisu

CDPRO Katsina Command

For: State Commandant

KASSAROTA DG Urges Citizens to Avoid Dumping Sand and Waste on Roads to Reduce Accidents and Ensure Safety in Katsina

KASSAROTA DG Urges Citizens to Avoid Dumping Sand and Waste on Roads to Reduce Accidents and Ensure Safety in Katsina

The Katsina State Road Traffic and Safety Authority (KASSAROTA) has called on the public to desist from dumping sand, soil, or waste on roads to minimize accidents and maintain cleanliness and safety on the state's highways.

In a statement issued by the agency's spokesperson, Abubakar Marwana Kofar Sauri, the Director-General of KASSAROTA, Major Rimi (Rtd), emphasized the importance of adhering to road traffic rules and regulations to ensure safety on the roads.

The DG stated that it is imperative for those washing motorcycles, tricycles, or cars on public roads to stop such activities as they violate established laws.

Furthermore, Major Rimi (Rtd) urged traders operating along roads and those displaying goods on pedestrian paths to ensure their activities do not obstruct movement or create congestion.

He also called on residents and vehicle owners in Katsina State to cooperate with KASSAROTA by following the rules set by the agency. He assured that the agency's officers would remain committed to ensuring safety and order on the roads.

The DG expressed gratitude to the Governor of Katsina State, Malam Dikko Umaru Radda (PhD), for his unwavering support towards the agency's success and commended the citizens for their cooperation.

Finally, he warned that anyone found violating the agency's laws would face penalties as prescribed by law. He reaffirmed the agency's determination to enforce regulations and ensure safety across the state.

Katsina Calls on Investors to Harness Mineral and Agricultural Opportunities


Katsina Calls on Investors to Harness Mineral and Agricultural Opportunities
Malan Dikko Umar Raɗɗa 

The Governor of Katsina State, Dr. Dikko Umaru Radda, has urged investors to explore the abundant opportunities in the state’s agricultural and mineral sectors.

Speaking at the opening of a one-day capacity-building workshop for exporters in Katsina, Governor Radda emphasized the state's untapped potential in agriculture, textiles, and minerals, calling for strategic efforts to maximize productivity and drive economic growth.

Themed “Unlocking Export Potential: Strategies for Success,” the workshop was organized by the Katsina State Investment Promotion Agency (KIPA) and held at the Munaj Event Centre in Katsina.

Governor Radda stated, “Katsina State is richly endowed with agricultural, textile, and mineral resources that remain largely untapped. By harnessing these resources, we can significantly boost our export portfolio and stimulate economic diversification.”

He further highlighted his administration’s commitment to creating a business-friendly environment, diversifying the state’s economy, and fostering sustainable growth and development.

Katsina Teacher Emerges Winner of Maltina National Teacher of the Year Competition 2023

Usman Yahaya Tama
Mallam Usman Yahaya Tama with Katsina State Commissioner of Education Hajia Hadiza Abubakar Yar'adua

The Honourable Commissioner Ministry of Basic and Secondary Education Katsina State, Hajiya Hadiza Abubakar Yar'adua, lauds the enormous efforts and warmly welcomes the Katsina State teacher who was named Maltina Teacher of the Year 2023 in the 9th edition.

BOA: Petition Against the Acting Managing Director, Bank of Agriculture

The Chairman, Friends of BOA Mr. Mahmud Badamasi has petitioned the acting Managing Director of the Bank of Agriculture Mr. Alwan Ali Alasan, over his alleged ineptitude, financial misdemeanor, and high-handedness.

World MSME Day 2020: Dikko Radda addresses the world

The DG Small and Medium Enterprises Development Agency of Nigeria [SMEDAN] Alhaji Dr. Dikko Umaru Radda
has today addressed a world press conference on the World MSME Day 2020

Brief Accounts of Suspension of Hajj in Islamic History

Around 40 times in history the Hajj was suspended or the number of pilgrims was extremely low according to King AbdulAziz Foundation For Research And Archives, and this idea is not as unprecedented as perceived

Police arrest coalition leader [CNG] for organising Katsina protest

The Nigerian Police have reportedly detained leader of the Coalition of Northern Groups, CNG, Nastura Ashir Sharif for organising peaceful protest in Katsina on Tuesday.

Banditry: Be patient with us - Buhari tells Katsina people

President Muhammadu Buhari has appealed to the people of Katsina State to be patient and supportive of the ongoing military operations in the state.

FLASH: Katsina Police Command declares notorious bandit wanted, places N5m reward

The Commissioner of Police, Katsina State command, CP Sanusi Buba, psc has today declared one Adamu Aliero Yankuzo wanted dead or alive.

Radda condoles with people of Katsina over recent killings

The Director General Small and Medium Enterprises Development Agency of Nigeria [SMEDAN] Alhaji Dikko Umaru Radda has condoled with people of Katsina over the recent killings in some parts of the state

I don't want any elective office in 2023 – Masari

Katsina State Governor Rt. Hon. Aminu Masari has declared that he would not seek elective office at the end of his second term in office in 2023

Gunmen killed another Village Head in Katsina

Gunmen  are reportedly said to have killed village head of Fafu in matazu Local Government Area of Katsina State last night

How Katsina Woman Regained Freedom After Six Weeks in Kidnapper's Custody

"Hadiza Garba said that, on that fateful day, five men each armed with AK-47 riffle stormed her house in Unguwar Bajida village of Yarmalamai ward and took her hostage"